MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

28 Jan 2014

MUTUWA DA KOWA KESO KYAKKYAWAN K'ARSHE

SHIN KO KASAN ALAMOMIN KYAKYAWAN CIKAWA?
Dukkan Musulmi na kwarai yana fatan yayi kyakyawan cikawa a lokacin da ze bar duniy. kuma ana iya ganin alamu da Nassin Hadisan Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya bayyana alamomin Suna dayawa, hakika Malamai Allah yayi masu Rahama sun bibiyesu suka sakamakon karanta Nassoshin dasuka zo akan haka, amma mu anan zamu kawo wasu ne daga cikinsu akwai:
* Furta kalman Shahada a lokacin mutuwa, kuma dalili akan haka shine Hadisi da Hakim ya ruwaito da waninsa daga Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: “Duk wanda karshen maganarsa yazama La ilaha illal lahu ze shiga Aljanna”.
* Mutuwa da Gumi na kwarara akan kumatu, wato yazama a kumatunsa akwai gumi a lokacin mutuwa, Saboda Hadisin da Buraida dan Hasib yaatuwaito cewa: Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: “ Mumini yana Mutuwane da gumi a kumatunsa” Ahmada da Tirmidhi.
* Mutuwa a ranar Jumu’a ko a darenta: Saboda fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: “Babu wani Musulmi daze mutu a ranar Juma’a ko a daren juma’a face Allah ya kareshi daga Azabar Kabari”.
* Yin Shahada a filin Yak’I saboda daukaka Kalmar Allah: ko ya mutu yana yaki saboda Allah ko ya mutu saboda rashin lafiya ta Annoba ko ciwon Ciki, ko ruwa yacishi Kuma dalili akan abubuwan da suka gabata shine Hadisin da Imamu Muslim daga Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: “ Wanene kuka kigawa cikin wanda sukayi Shahada a cikinku? Sukace: Wanda aka kashe saboda Allah shine wanda yayi Shahada, Yace: kenanan masu yin Shahada a cikin Al’ummata yan kad’an ne. se Sukace: To su wanene Ya Manzan Allah? Yace: "wanda aka kashe saboda Allah yayi Shahada, wanda ya mutu akan tafarkin Allah yayi Shahada, wanda ya mutu saboda Annoba yayi Shahada, wanda ya mutu saboda ciwon ciki yayi shahada, da wanda ya mutu saboda ciwon ciki yayi shahada, da wanda Ruwa yaci yayi shahada”.
* Mutuwa saboda Rushewar Gini: Saboda Hadisin da Imamul bukhari da Muslim suka ruwaito Daga manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: “ Wadanda sikayi mutuwan Shahada su biyar ne: “ wanda aka Soka da Mashi, da Me ciwon Ciki, da wanda ruwa ya Nutsa dashi, da wanda Gini ya fad’a ma, da wanda Yayi shahada saboda Allah”.
* Mace ta mutu a lokacin haihuwa saboda d’anta ko ta mutu dashi a ciki, kuma dalili akan haka shine ingantaccen Hadisin da Imamu Ahmad ya ruwaito daga Ubbadatu dan Samit cewa: Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Ya bada labarin masu shahada se ya ambata a cikinsu: “Macen da danta ya kashe ta….. danta ze jawota zuwa Aljanna da cibiyarsa” wato ze da igiya ta ikon Allah wanda ake yanke masa.
* Konewa da wuta : dalilin haka shine Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Ya ambaci adadi na masu shahada se ya ambaci wanda wuta ta kona..........................
* Mutuwa da ciwon rashin lafiya, Annabi Sallallahu Alaihi Wasllam Yabada labarin hakan, cewa Shahada ce.

23 Dec 2009

Cutarwan Shan Taba

Shan Taba YA watsu a ko'ina , kuma yawan masu Shan Taba ya kara yawa a wannnan zamani , abinda ake tsoron karuwan matsaloli tsakaninsu , bincike da yawa sun nuna cewa Shan Taba na cutar da lafiya da hatsari masu yawa , kuma yana haifar da Cututtuka masu hatsari , daga ciki akwai : Cututtukan Zuciya , da Kansan Huhu ( Lung Cancer ) , Pneumonia , Haka yana Sanya tsufa da wuri , Kuma Yana Kara yawan adadin masu mutuwa ( Mortal rates ). Zamu cigaba insha Allah

28 Feb 2009

DARUSSA GAMEDA DOGEWA TA GAZZA

DARUSSA GAMEDA DOGEWA TA GAZZA Duk da wadanda suka saba da rub utu kuma ni daya ne daga cikinsu suyi iyo a kogi me girma na baiwa abubuwa muhimmanci, kuma suyi Magana da yawa kuma suyi rubutu da yawa wani lokaci suyi suka , wani lokaci su yaba wani lokaci sukan karfafa ma wasunsu gwuiwa. So dayawa me rubutu yana sake ma alkalaminsa……………………………

HADA ALAH DA WANI (SHIRKA)

SHIRKA

Shirka itace mafi girman abinda Allah ya haramta aayan kasa , Saboda Hadisin da Abi Bakrata ya ruwaito Yace : Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: "Shin bana baku labarin mafi girman Manyan laifuka ba har sau uku Se Sahabbai sukace bamu ya Manzan Allah , se Manzan Allah Yace: Shine Yin Shirka da Allah…" Bukhari No. 2511.

Haka kowani laifi Allah ze iya gafartawa me shi in banda Shirka domin ita se anyi mata tuba kebantatta Allah Madaukakin Sarki Yace: ( Lallai Allah Madaukakin Sarki baya yin gafara ga wanda yayi Shirka dashi , amma yanayin gafara ga abinda ba Shirka ba ga wanda yaso ) Sur. An Nisa'i – 48.

Kuma daga cikin Nau'ukan Shirka , akwai Shirkan da take fitar da mutum daga Musulunci , kuma me ita ze dauwama a cikin Wuta matukar ya mutu yana aikatawa.

Kadan daga cikin wannan Shirkan data watsu a garuruwan Musulmi akwai :- Yin Bauta ga Kabari…...

YIN BAUTA GA KABARI

Kudurin cewa Waliyyan da suka mutu suna biyan bukatu , kuma suna faranta bakin ciki , da neman temakonsu da neman cetonsu , Allah Madaukakin Sarki Yana Cewa: (Kuma Ubangijinka yayi hukunci cewa kada ku bautama wani inbanda shi) Sur.Al'isra'I – 23. haka kuma kiran Annabawa da Mutanen kwarai dasuka mutu ko waninsu dominsu cecesu , ko su kubutar dasu daga tsanani. Bayan Allah Madaukakin Sarki Yana cewa: (Wanene wanda yake amsaa ma mabukaci idan yakirashi , kuma yake yaye bakin ciki , kuma ya sanya ku halifofi akan kasa, shin akwai wani abin bauta in banda Allah?) Sur. Naml -62.

Wasunsu kuma zasu riki sunan wani Shehi ko Waliyyi idan zasu tashi ko zasu zauna ko idan sunyi tuntube ,kuma duk sanda suka cikin wani hali na bala'I ko bakin ciki , se kaji wannan yana cewa Ya Muhammad! , wancan sekaji yana cewa Ya Aliyyu ! , ko Ya Husaini! , ko wancan YAce Ya Badawi ko Ya Jilani , wannnan na fadin Ya shazali! , ko ya Rufa'I , wani kuma na kiran Ya Saidarus! Ko Ya Saiyada Zainab , wani kuma na kiran dan Alwan bacin Allah madaukakin Sarki Yana Cewa: ( Lallai wadannan da kuke kira Wanda ba Allah ba bayi ne kamanku) Sur. Al'a'araf – 194.

Wasu kuma da suke bauta ma Kabari zakaga suna kewayashi –wato suna masa dawafi- kuma kaga suna sumbantan rukunnansa kaga suna shafe jikinsu dashi , kuma suna smbantansa, kuma sun abaca baca da kasa a fuskokinsu , kuma suna makabarin sujjada , kaga sun tsaya a gabansa suna masu cike da tsoro da kaskantar dakai suna rokon biyan bukatunsu , na neman warkar da mara lafiya , ko neman Haihuwa ko sauwake wani abu , kai zakaji wani ma yana kiran wand ke cikin kabari yana cewa Ya Sayyidi - wato Shugabana- nazo maka daga gari me nisa kada ka bani kunya. Allah Madaukakin Sarki kuwa Yana Cewa: ( Shin wanene yafi bata fiye da wanda ya kira wani wanda ba Alah ba , wanda baya karba masa har zuwa tashin Alkiyama , kuma alhali su rafkanannu ne gameda rokonsu da'akeyi musu) Sur. Al'ahkaf – 5. Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: " Duk wanda ya mutu alhali yana rokon wani wanda ba Allah a matsayin kishiya ze shiga Wuta" Bukhari. Wasu daga cikinsu zakaga suna aske gashin kawunansu a wurin kabur-buran , wani daga cikinsu ya wallafa Littafi ne me taken (Manasiku Hajjil Mashahid) Ma'ana Ayyukan Hajjin Kabur – bura na Waliyyai kenan , wasu kuma suna da Kudurin cewa Waliyyai sunayin tasarrufi a duniya wato suna zartar da wasu abubuwa dake faruwa , suna Cutarwa suna amfanarwa Alhali kuwa Alah Madaukakin Sarki Yana cewa: (Kuma idan Allah ya sanya maka wani Ciwo to babu me yaye maka in bandashi kuma idan yayi nufinka da wani Alkhairi to babu me mayar da Wannan Falalar) Sur. Yunus – 107.

Kuma Yana daga cikin Shirka Yin Alwashi ga wanda ba Allah ba kamar yanda wasu sukeyiwa wasu kabur bura awashi. Allah ya Shiryamu.

zamu cigaba insha Allahu.

*** Yana daga cikin Babban Shirka Yin Yanka ga wanda ba Allah ba , Allah Madaukakin Sarki Yana cewa : (Kayi Sallah ga Ubangijinka ka kumayi Yanka) Sur. Alkauthar -2. abin nufi kayi yanka dan Allah kadai kuma da sunansa , Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: " Allah ya La'anci wanda yayi Yanka ga wani wanda ba Allah ba" Imamu Muslim.

Kuma aikata haramun guda biyu zasu iya haduwa ga abin Yanka sune: Yin Yanka badan Alah ba , sannan YinaYankan bada sunan Allah ba , kuma dukansu abubuwa ne dasuke hana cin Yanka. Kuma akwai Yanka na Jahiliyya wanda ya watsu a zamanin mu shine " Yin Yanka saboda Aljanu" sun kasance idan suka saya gida ko suka gina gida ko suka haka rijiya se suyi Yanka a wajen ko akan kofar gidan ko rijiyar domin tsoron cutarwar Aljanu

23 Sept 2008

I'ITIKAFI

Dasunan Allah mai Rahama Mai Jinkai

Shine lazimtan masallaci da zama cikinsa da niyyan samun kusanci zuwa ga Allah. kuma malamai sunyi ittifak'I -wato sun hadu- akan cewa itikafi an shar'antashi kuma mustahabbi ne.

Tunatarwa: wasu mutane na kuskure ta yanda suke daukan cewa Itikafi, yakebanci manzan Allah ne Sallalahu Alaihi Wasallam shi kadai, wasu kuma suce hadisin Itikafi an shafe shi, wasu kuma suna dauka cewa Itikafi na dattawane ko akasin hakan, to duk wadannan kurakurai ne ba'a sha. Nana A'isha Allah yakara yarda agareta tace: (Lallai manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yanayin Itikafi a cikin goma na K'arshe na Ramadan har Allah yadauki ransa, sannan matansa sukayi Itikafi a bayansa) Bukhari. Ibn Hjar yace (Ba'a shafe hadisin ba kuma baya cikin abubuwan da suka kebanci ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam)fathul baari 4/272.

HUKUNCIN ITIKAFI

Mafi yawan malamai sun tafi akan cewa mustahabbi ne.

Imamu Malik Yace: (Nayi tunani akan al'amarin Itikafi, da abinda yazo akansa, da yanda musulmai suka barshi, tareda cewa manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be kasance yabarshi ba, se naga cewa sun barshi ne saboda yanada wahala akansu.)

Imam Azzuhri Yace: (akwai mamaki a Al'amarin musulmi! Sun bar Itikafi, tareda cewa Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be barshi ba tunda yazo Madinah , har Allah madaukakin Sarki yadauka ransa.)

SHARUDDAN ITIKAFI

1. MUSULUNCI: baya inganta ga wanda ba musulmi ba.

2. HANKALI: mahaukaci baya itikafi, saboda koda ibada ta wajibi bata zama dole akansu ba, andaga alkalami akansu.

3. NIYYA: sharad'I ce ga dukkan ibadodi, kuma duk aikmin da babu niyya a cikinsa ba karbabbe bane.

4. MASALLACI: ga namiji dolene yayi a masallaci, amma mace kuma anyi sabani akanta, Malam SUHNUNU Yace: (nace ma ibnul K'asim: menene zancen Imamu Malik gameda Itikafin mace tayi amasallacin jama'a? se yace Na'am, yace: a zancen Malik tayi Itikafi a masallacin gidanta? Se yace: Hakan baya burgeni, ana itikafi ne a masallacin da'aka yishi dan Allah.) Mudawwana 1/295.

Sheikh Aminul Hajj yace: (amma yafi rinjayen dalili awurina shine mace tayi Itikafinta a gidanta, wato wurin da takebance shi tana sallah a cikinsa.

5. AZUMI: wasu daga cikin malamai sukace kada mutum yayi itikafi face yaname Azumi, an tambayi Ibnul K'asim: (shin anayin itikafi batare da azumi ba a cikin zancen Malik? Se yace: ba'ayi se da Azumi. Wasu kuma sukace anayi koda mutum beyi Azumi ba, Sukace wannan shine ra'ayi mafi rinjayen dalili, saboda Hadisi Umar ingantacce da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya Umarce shi da yayi itikafi yayin da yace masa yayi alwashin yin hakan a jahiliyya, kuma be ce masa yayi Azumi ba.

6. IZINI: dolene se miji yayi wa matarsa izini ko abinda ya mallaka na bawa ko baiwa, miji mace yana gida ne ko yayi tafiya dole tanemi izininsa, kuma idan yayi mata izini, to be kamata ya hanata ba kuma.

RUKUNNAN ITIKAFI

1. Zama a cikin Masallaci. 2. Nisantan Jima'I da abubuwan da zasu iya kaishi yin hakan. 3. Nisantar manyan laifuka. 4. Musulunci. 5. Hankali. 6. Tsarki daga Haila. Itikafi yana baci saboda rashin daya daga cikin wadannan.

ABUBUWAN DASUKE BATA ITIKAFI

1. FITA DAGA MASALLACI: baya halasta fita daga masallaci, In banda fita saboda: dan Biyan bukata kamar fitsari ko bayan gari, wankan janaba da na jumu'ah, cin abinci ko abin sha idan be iya ci ko sha a wurin da yake itikafi, idan yaji tsoron wuta ko sata kom rushewan gini, in aka fitar da shi da karfi, idan mace tayi haila da sharadin ta dawo da tayi tsarki, idan mijin mace yarasu ko yasake ta zata fita a mafi rinjayen zancen malamai biyu wasu sukace zata cigaba har seta kammala, fita saboda yin Umara, fita da mantuwa, idan yayi hauka ko suma.

2. YIN JIMA'I: saboda Allah yace: (kuma kada ku sadu dasu, alhalin kuna masu Itikafi a cikin masallatai…) Sur.Baqarah-186. haka sun bantan mace da sha'awa.

3. YIN RIDDA:wato fita daga musulunci

4. YIN MANYAN LAIFUKA: kamar yin zina da sata acikin itikafi, wanda mutane suna sakaci da daukan abin wani ko da kadan kuwa se a kiyaye.

5. YIN HAUKA KO SUMA: yana bata itikafi se dai idan yasami lafiya ko ya farfad'o to se yacigaba.

6. HAILA: idan mace tayi haila itikafinta ya baci, amma idan tayi tsarki se ta cigaba, na bayan be baciba.

ABUBUWAN DA BA'ASO GAME ITIKAFI

Ba'aso me itikafi ya shagaltu da abinda ba ambaton Allah ba, da kuma abinda ba dolene ba.

1. jayayya. 2. zagi damaganganun banza. 3. Yin giiba da Annamimanci. 4. Kallon abinda yake haramun. 5. Rashin yin magana gaba daya tun daga safe har dare da sunan bauta.

Tunatarwa: wasu daga cikin daliban ilimi se kaga suna zuwa itikafi da wasu littafai na karatunsu suna yin muraja'a, ba haramun bane amma kamata yayi tunda kwanakine yan kadan a cikin shekara, meze sa bazakayi hakuriba, sauran kwanakin shekara kayi acikinsu.

ABUBUWAN DASUKA HALASTA GAME ITIKAFI

1. Yin wanka da canza kaya, da sanya kayan da yakeso.

2. Cin Abinci da Shan Abin Sha a cikin masallaci.

3. Yin magan da yan uwa, amma ba'ason yawaita surutu da mutane.

4.Ya nemi Aure ko a daura masa Aure.

5. Yin Aski da yanke Farce.

6. Sanya turare.

ABUBUWAN DA SUKE MUSTAHABBI GA ME ITIKAFI

1. Mustahabbi ne ga me itikafi, yakafa tanti da ze kangeshi daga jama'a, inbe samu ba se ya lazimce wurin da babu jama'a ta yanda baze barshi ba seda larura.

2. kiyaye yin Sallah cikin jama'a, da nafiloli.

3. Yawan karatun alk'ur'ani, da rashin shagaltuwa da abinda ba ruwa.

4. Yawan ambaton Allah, zikiri, da tasbihi.

5. Yin azumi a cikin wantan da ba ramadan, ga wanda zeyi itikafi da rana.

6. Yawan yin kokari wajen d'a'a.

MAFI KARANCIN ITIKAFI DA MAFI YAWANSA

Itikafin neman lada baya da kad'an ko mafi yawa, se dai wanda yayi Itikafi a goman k'arshe na Azumin kada ya fita se idan anga watan Sallah wato Shawwal, malamai sun hadu akan cewa baya da mafi yawa, amma sunyi maganganu akan karancinsa, wasu sukace mafi karancinsa Sa'a, wasu sukace Yini daya da dare, wasu sukace kwana goma.

Imamul k'urtabi yace: ( mafi karancin itikafi a wajen Malik, da Abu Hanifa, dare da yini….)

YAUSHE AKE SHIGA ITIKAFI KUMA YAUSHE AKE FITA

A. Shiga wajen itikafi:akwai zancen malamai guda biyu:

1. Shiga bayan sallar Asubahin ranar Ashirin da d'aya na Ramadan, saboda hadisin Nana A'isha Allah yakara mata yarda tace: (Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam idan ze shiga itikafi yana yin sallar Asubahi, sannan se yashiga wurin itikafinsa) Bukhari. kuma wannan shine mafi rinjayen dalili. Kuma mazhabinAhmad da Laith da Ishak'.

2. Shiga kafin rana r daren Ashirin da d'aya ta fad'i, wannan shine mazhabin Malamai hud'u

B. Fita daga itikafi: Ana fita daga wurin itikafi bayan ganin watan sallah, wasu kuma sukace mustahabbine ya bari har yayi sallar idi sannan ya tafi.

SIRRIN DA YAKE CIKIN I'ITIKAFI

Bauta tana da sirruka da hikimomi masu yawa, saboda ayyuka gaba daya, makewayansu itace Zuciya, kamar yanda Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace (..Kusaurara! lallai acikin jiki akwai wata tsoka wanda idan ta gyaru, to dukkan sauran jiki ya gyaru, kuma idan ta bace, to dukkan Sauran jiki ya baci, ku saurara! Itace zuciya.) Bukhari da Muslim.

To in muka duba zamuga cewa mafi yawan abubuwan da suke bata zuciya, sune sha'awan cin abinci da abin sha da saduwa da Iyali da Zancen da ba na dole ba, da barcin da ba na dole ba, da abokai da basu da wata fa'ida da sauran abubuwa dasuke kawar da zuciya daga yin abinda yake biyayya ne ga Allah, se Allah ya Shar'anta wasu abubuwa na lada da zasukare zuciya daga rud'ani da shagaltuwa daga ambaton Allah, kamar Azumi wanda yake hana mutum cin abinci da abin Sha da Saduwa da Iyali da rana. To wannan hanuwan daga wadannan abubuwan jin dadi, shine yake karfafa alak'a tsakanin mutum da Ubangijinsa, da fuskantar dashi ga Lahira, kena Azumi garkuwa ce datake kare zuciya daga abubuwan sha'awa da suke kawar da mutum daga yin biyayya ga Allah, duk da hanine wanda yake matsakaici saboda an halasta wa mutum wadannan abubuwa a cikin dare.

To haka shima Itikafi yanada Sirri me girma, shine Kare mutum daga yawan cakud'a da jama'a, da yawan magana, saboda me Itikafi yana shagaltuwane da karatun Alk'ur'ani da Tsayuwa –wato yin sallah- da Zikiri da yawan yin Addu'a da makamantansu, haka kuma akwai kariya daga yawan barci, tunda yazo ibada ne ba barci ba, to wadannan abubuwa barinsu shike kara sa zuciya ta fuskanci Allah.

ABUBUWAN TUNATARWA

* Wasu daga cikin malamai sun tafi akan cewa ba'ayin Itikafi se a masallatai guda Uku kamar yadda yazo a cikin Hadisi, na hani akan yin Itikafi a masallatan da basuba, manzan Allah Sallalahu Alaihi Waasallam yace (Babu Itikafi face a masallatai guda uku) imamu Tahawi. -Wato masallacin Harami wato Ka'abah da masallacin Madinah da masallacin Aqsa wato Kudus-, Malamai suka fassara shi da cewa hani ne na yin alwashin yin Itikafi a wani masallaci da tafiya zuwa gareshi saboda hakan se a wadannan masallatan kadai ya halatta, ayi hakan saboda duk malaman mazhabobi Hud'u sun hadu akan cewa ya halatta ayi a kowani masallacin Juma'a.

* wasu sukan bar ayyukansu na wajibi saboda suyi Itikafi, to yin hakan kuskure ne saboda shi Itikafi sunna ce, saboda haka ba'a barin abinda yake wajibi saboda Sunnah.

Ya Allah Ka Karba mana dukkan Ayyukanmu a cikin Watan Ramadana kasa Muna cikin Bayinka Yantattu dag Wuta kuma kadatarmu da daren Lailatul K'adari. Amiin

15 Sept 2008

SADUWA DA MATA CIKIN HAILA

SADUWA DA MATA CIKIN HAILA

Allah Madaukakin Sarki Yace: ( Kuma Suna tanbayarka game da Haila , Kace kazanta ne , Ku Nisanci Mata a cikin Haila , kuma jada ku kusance su har se sunyi tsarki) [Suratul Baqarah - 222].

Saboda haka baya halatta wato Haramun ne Mutum ya kusanci matarsa har se tayi wanka bayan tsarki , saboda Fadin Allah Madaukakin Sarki: (To idan Sunyi tsarki Se kuzo masu ta inda Allah Ya Umarce ku…)[Suratul Baqarah - 222].

Kuma abinda ke nuna munin wannan Laifi Shine Hadisin da Abu Hurairah Yace: Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: (Duk Wanda yazo ma me Haila , ko yazo ma mace ta bayanta , ko yaje wajen Boka , to ya kafirta daga abinda aka Saukar wa Muhammad) [ Imamu Tirmidhi-Vol.1- 243].

Ma’ana wanda ya sadu da matarsa alhali tana cikin Haila , ko ya sadu da ita ta wurin bayan gidanta. To duk wanda ya aikata hakan da kus – kure , bada gan – gan ba , alhali be sani ba , babu komai akansa , wanda kuma ya aikata hakan dagan - ganci yana sane , To zeyi kaffara a daya daga cikin zantukan Malamai wanda sukace hadisin kaffara ya inganta , shine yayi sadaka da Dinar wato Zinare ko rabin Zinare , Wasu sukace yanada zabi cikinsu wato kodai ya bada Zinare ko rabinsa , Wasu Malaman Sukace: Idan yazo mata a lokacin da ta fara Haila to ze bada Zinare cikakke , idan kuma a karshen Hailan yazo mata wato lokacin da jinin ya ragu ko kafin tayi wankan Haila to ze bayar da rabin Zinare. Zinare cikakke kuma ana kwatantashi da 4.25gram ko da kudin da ake sayar dashi. Sannan abinda Malamai sukace shine dai – dai shine Zance da’akace yanada zabi tsakanin zinare ko rabinsa.

31 Aug 2008

DARUSSAN AZUMI NA (1)

Dasunan Allah Me Rahama Me Jinkai
ME ZAMU KOYA NA DARUSSA A CIKIN MAKARANTAR AZUMIN RAMADAN?
Godiya ta tabbata ga Allah , tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga shugaban halittu , Muhammad Sallallahu Alaihi Wasalam , wanda aka saukarwa da Alkur'ani a cikin watan Ramadan da Iyalan gidansa , masu tsayuwan dararen , da Sahabbansa wadanda suka kasance suna raya dare da Yinin Ramadan da ibada.
Watan Ramadan da irin falalar da Alah yasanya a cikinsa , da abubuwan da'aka shar'anta a cikinsa na ayyukan lada ana daukarsa a matsayin Makaranta ce da Mumini ze samu mafi daukakan ilimomi , daga ciki akwai mafi girman sani , ta yanda koda Ramadana ya wuce – wato yakare kenan zebar wadansu alamomi ga Mumini , saboda ribatuwa dayayi da wannan watan.
TO YAZAMUYI MUSANYA RAMADAN YAZAMA MAKARANTA GA RAYUKANMU?gasu kamar haka:-
NA FARKO:- JIN TSORON ALLAH:
Azumin Watan Ramadan yana daga cikin mafi girman dalilan dake tsarkake Rai , duk wanda ya Azumce shi yana me Imani dashi da kwadayin lada Ransa zata tsarkaka , tayi danshi , kuma ta kubuta daga abubuwan da'aka haramta da Sabo. To Wanke Rai da tsarkaketa , dayane daga cikin mafiya girman manufofin Azumi. Allah subhanahu Wata'ala Yace:- ( Yaku Wadanda sukayi Imani , an wajabta maku yin Azumi , kamar yadda aka wajabta akan wadanda suka gabace ku , domin kusami takawa –wato tsoron Allah-) [Sur. Baqarah- 183].
Shaikh Sa'ady a cikin Tafsirinsa Yace: " Ambaton Allah ga Azumi fa'ida ce me girma wacce take kunshe cikin Fa'idodi masu yawa , fadansa ( domin kusami jin tsoron Allah)
Ma'anarsa Azumin yazama hanyace agareku wajen samun jin tsoron Allah , kuma domin ku kasance a cikin masu jin tsoron Allah ta dalilin Azumin , saboda haka jin tsoron Allah sunane daya kunshi dukkan abinda Allah yakeso , kuma ya yarda dashi , na aikata abubuwan da Allah da Manzansa suka wajabta da barin dukkan abinda Allah da Manzansa suke ki , saboda haka Azumi hanyace mafi girma dan cimma wannan gaya me girma, wacce take kai bawa zuwa ga jin dadi da tsira.
Lallai me Azumi yana samun kusanci zuwa ga Allah da barin abinda Ransa takeso na abinci abin Sha da makamantansu , gabatar da Son Allah akan Sansa ga kansa.
Sannan Jin tsoron Allah shine Farkon darasi da me Azumi ze samu saboda haka dole ne yakiyaye hakan , Mumini me Azumi me neman lada baya sanya burinsa da himmarsa wajen samun jin tsoron Allah a cikin kwanakin Ramadana kadai , A'a niyyarsa tafi haka , shi dai yana yin Azumin Ramadana ne domin ya sabunta alkawari tsakaninsa da Alah , Alkawarin yin bauta tsarkakka ga Allah , wanda gabobinsa suna Azumin da kamewa daga sabon da Rai takeyi , kuma ya sabunta Alkawari da tuba , kuma ya karfafa himmarsa akan cigaba da yiwa Allah biyayya har zuwa mutuwa , To wannan shine wanda ya fahimci manufar Ramadan , wanda be takaita Jin tsoron Allah dayakeyi akan watan Ramadana kadai ba , A'a Jin tsoron Allah na cigaba har abada.